September 18, 2026

Fim Ɗin IGIYAR ƘASA Zai Kawo Sauyi A Masana’antar Fim Ta Jamhuriyar Nijar.

0

Daga MUKHTAR YAKUBU.

A daidai lokacin da a ke ganin harkar fim ta sauya sabon Salo a duniya ta fannin ci gaba da fasahar zamani, sau da yawa su ma masu gudanar da harkar fim a Jamhuriyar Nijar sun yi wani yunkuri na samar da wani fim da za a iya cewar zai iya sauya salon finafinan su zuwa daidai da yadda a ke gudanar da fim a duniya.

Babu shakka fim ɗin IGIYAR ƘASA da aka yi shi a Ƙasar Nijar wanda bayan kammala shi a yanzu yake dab da fara nuna shi a manyan gidajen Talbijin da Sinimu fim ne da ya samu aiki mai inganci wanda hakan ya sa a ke ganin zai kawo sauyi a Masana’antar fim ta Jamhuriyar Nijar.

Babban Furodusan fim ɗin Saminu S Turaki a tattaunawar da suka yi da wakilin Popular News Hausa ya bayyana mana cewar sun daɗe da tunanin shirya fim din amma saboda ana son a tabbatar da an yi aiki mai inganci ya sa suka ɗauki lokaci mai tsawo suna shiryawa kafin su shiga aikin wanda kuma a halin yanzu an kai ga shirya kashi na farko.

Ya ci gaba da cewa “Duk da mun samu nasarori masu yawa amma mun samu ƙalubale, domin shi fim wani abu ne da za ka shafe tsawon lokaci kana aikin sa amma wani idan ya zo kallo cikin Sa’a ɗaya sai ya kushe maka shi, domin ko samar da labarin fim ɗin abu ne da mun ɗauki wajen shekara goma wanda a farko fim ɗin ya fara daga na Sa’a ɗaya ne.

Amma da yake kullum ana ƙara samun ci gaba a harkar fim sai ya zama lokacin da za mu yi aikin ya zo lokacin da a ke yayin fim mai dogon zango, don haka sai muka tafi da zamani muka yi shi a tsarin don haka a yanzu mun kammala muna shirin haska shi domin duniya ta ga irin Ƙyaƙyawan aikin da muka yi”

Shi ma Daraktan fim ɗin Basirou Garba ya shaida mana cewar ” A matsayina na wanda na rabuta labarin kuma na tsara sannan na zo na yi aikin bada umarni na san kowanne aiki zaman kan sa yake yi amma da yake ni mutum ne karance karance hakan ya ba ni dama wajen cimma nasara a wannan aikin na IGIYAR ƘASA”.

Dangane da yadda labarin ya zo da wani sabon Salo kuwa cewa ya yi”To gaskiya wani sako ne muke so mu isar don haka muka shigar da Maciji cikin labarin don na san mutane za su ga wani sabon abu, to daman shi fim a kullum ana son a samar da sabon salo na isar da sako wanda zai ja hankalin masu kallon shi ya sa muka samar da wannan fim na IGIYAR ƘASA.

Kuma muna son mu sanar da mutane alaƙar mutum da sauran kwari duk wanda ya kasance ba ya cutar da Ɗan adam to bai kamata a kashe shi ba, saboda kashe shi ɗin wani lokacin zai iya haifar da wata matsala kamar Kadangare da makamantan su da ba sa cutarwa wanda idan aka kashe su wani lokacin suna ɗaukar fansa saboda wasu suna da Alaƙa da aljannu to sai muka gina labarin a kan Maciji wanda shi bai cutar ba sai aka cutar da shi, don haka sai ya tafi neman fansa”

An dai yi aiki mai inganci wanda ya fito da sakon da a ke so a isar. Su kan su jaruman sun yi abin da ya dace kamar daman su samu horo na lokaci mai tsawo. Abin jira dai a gani shi ne buƙatar kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *