September 18, 2026

EFCC Ta Ja Kunnen Yan Najeriya Su Daina Sayar Da Kuru’u.

0

Hukumar dake bankado masu yima tattalin arzukin Najeriya zagon kasa ta ja kunnen yan kasa dasu daina saye ko saida kuri’arsu a lokacin zabe.

Sakataren hukumar Dr. George Epungu ya yi wannan kiran jim kadan da amsar wata tawagar kungiyoyin fararen hula masu fafutukar yi ma zabe garanbawul a lokacin da suka kai ma hukumar ziyarar ban girma a Abuja.

Sakataren hukumar ya yaba ma kungiyoyin bisa zuwa su mika bukatarsu ta neman yin hadin gwiwa da hukumar don ganin an shawo kan matsalar ta saye da sayar da kuru’u a cikin kasar nan.

Shugaban tawagar Anyodare Atoye ya ce sun zo ne don yin hadin gwiwa da hukumar a magance wannan matsalar dake faruwa a lokacin zabe.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *