September 16, 2026

An Buɗe Gasar Cin Kofin Baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina.

0

An Buɗe Gasar Cin Kofin Baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina.

An buɗe gasar kwallon kafa ta cin kofin baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina domin tayashi murnar cika shekara a ofis.

Gasar dai na da nufin ƙara kyautata alaƙa a tsakanin matasa inda kulob 32 za su fafata a fili wasa na birget na 17 da kuma filin wasa na KCK da ke Katsina.

Tunda farko da yake jawabi a taron bikin buɗe gasar baban kwamanda mai kula da Birget na 17 da ke Katsina Ibikunle Ademola Ajose ya bayyana cewa shirya irin waɗannan wassani abu ne kyau domin ta haka ne za a ƙara kulla alaƙa a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka shirya wannan gasa sun yi hangen nesa, kuma sun yi abinda ya kamata a lokacin da ya kamata musamman tunawa da shi babban Hafsan Sojojin Nijeriya Christopher Gwabin Musa

A cewar baban kwamanda mai kula da birget na 17 Ibikunle Ademola yana fatan za a yi wannan gasa a kammala cikin nasara ba tare da wata matsala ba musamman tunda abin ya haɗa da matasa.

A wajen wannan biki dai an shirya cewa kungiyoyin kwallo guda biyu ne za ƙara wato Sarkin Yaki da kuma K-Soro , wanda kuma aka fafata daga ƙarshe kungiyar kwallon kafa ta K-Soro ta samu nasara bayan an yi bugun daga kai sai mia tsaron gida.

Yanzu dai za a cigaba da waɗannan wassani a fili wasa na KCK inda ake sa ran sauran kolab ɗin za su nuna bajintar su domin samun nasara a ƙarshen gasar.

Shima da yake nasa jawabin shugaban shirya wannan gasa domin taya baban Hafsan Sojojin Nijeriya Janar Christopher Gwabin Musa Malam Lawal BK ya bayyana cewa sun yi tunanin shirya gasar ne domin sada zumunci a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa yanzu hanya mafi sauki da za a ja matasa a jiki ita ce shirya irin wannan gasa, ya ce ba komi, ka ɗora matasa a wata turba wanda zata hana su yin tunanin abubuwa marasa kyau.

“Matasan mu yanzu idan ka kyale su, ba zamu yi tunanin irin wanda ya kamata ba, amma shi wasan ƙwallon ƙafa abu ne da matasa ke so, to ko ba komi ka ɗebe masu kewa sannan ka sanya su nishadi ” inji shi

Kamar yadda aka tsara kungiyoyin kwallo kafa guda 32 ne za su fafata kuma wasa daya ne za a riƙa bugawa duk wanda ya samu nasara zai hau mataki na gaba.

Kazalika an ware kyaututtuka masu yawa wanda a ƙarshen gasar za a rabawa kungiyar da ta samu nasara.

Sauran kungiyoyin kwallon kafar da za su taka leda sun haɗa da Katsina Boys da Shooting Star da Durbi Strikers da KKT Strikers da Home Boys da Gawo Prof. da kuma Kamuwa United da Manoco ATC da dai sauransu.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *