Zaɓen 2023: Shiyyar Kudancin Yobe Sun Buƙaci Sanata Bomai Ya Maimaita
Daga Muhammad Maitela, Damaturu
Al’ummar kudancin jihar Yobe (Zone B) sun bayyana gamsuwarsu dangane da wakilcin Sanata mai wakiltar shiyyar a zauren majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ibrahim Mohammed Bomai, wanda sakamakon hakan kungiyoyi daban-daban a yankin su ka shirya taro na musamman domin nuna cikakken goyon bayan su tare da kira ya sake fitowa don maimaita kujerar sa.
Kana da ƙaddamar da gidauniyar da suka tara naira miliyan 45 domin saya masa fam din takara a zaɓen 2023 mai zuwa.
Yayin da dubban jama’a suka gudanar da wannan taron a babban dakin taro na Kwalejin Ilimi ta Gwamnatin Tarayya (Federal College of Education- Technical) da ke Potiskum don nuna wa sanatan goyon baya a zaɓe mai zuwa na 2023.
Bugu da ƙari, nan take kungiyoyin suka haɗa wa Sanata Bomai naira miliyan 45 domin saya masa fam, wanda daga bisani suka garzaya zuwa sakatariyar jam’iyyar APC da ke Abuja domin sayen fam ɗin ga Sanatan.
Kungiyoyin da suka bayar da gudumawa mai tsoko a asusun sayen fam din sun haɗa da ‘Yobe South Movement for Good Governance’ da ‘National Association of Automobile Technicians’ (NATA), sai ‘Ma’ina Kara’, tare da kungiyar ‘Mbeno Association’, Students Union and National Union of Road Transport Workers’ (NURTW) da makamantan su.
Da yake jawabin ƙaddamar da taron tare da tara kuɗin sayen fam, Ko’udinatan ‘Bomai Movement’, Alhaji Muhammad Buhari Yusuf ya bayyana cewa Sanata Bomai ya bayyana cewa Sanatan ya fitar musu kitse a wuta, kuma ya ce kawowa yanzu kwalliya ta biya kuɗin sabulu, ya ƙara da cewa, “wannan taron yau kadai ya tabbatar da cewa ‘gani ya kori ji’ musamman irin yadda al’umma ta fito kwansu da kwarkwata wajen nuna cikakken goyon baya tare da buƙatar Sanata Bomai ya maimaita.”
A nashi ɓangaren ngaren, Barrister Khalil Halilu ya zayyana wasu daga cikin nasarorin da Sanatan ya samar a kudancin jihar Yobe, wanda suka taɓa kowane ɓangaren ci gaban jama’a.
Bugu da ƙari, shima shugaban jam’iyyar APC a ƙaramar hukumar Potiskum, Alhaji Bala Musa Lawan ya tofa albarkacin bakin sa dangane da ci gaban da yankin ya samu ta dalilin muhimman ayyukan inganta rayuwa da Sanata Bomai ya samar, ya ƙara da cewa, “Sanata Bomai shugaba ne nagari wanda ya tattaro siffofin shugaba mai hangen nesa tare da kaunar al’ummar sa. Wanda bisa haka me muke kira gareshi ya maimaita kujerar shi a 2023.”
Abubakar Baba Dada, a taron ya fassara kokarin da Sanata Bomai ya yi wa yankin sa a matsayin abin da sun zarta a fada cikin karamin lokaci, “Saboda haka zamu ci gaba da hada kan jama’a domin nema masa karin goyon baya, domin ci gaba da samun karin muhimman ayyukan ci gaba.”
Shi kuma Yusuf Zaki, mai magana da yawun kungiyar al’ummar Kare-Kare (Ma’ina Kara Association), dangane da bayar da kyautar naira miliyan 5 da kungiyar ta yi a matsayin goyon baya ga Sanatan.
