September 18, 2026

Dan Takarar Gwamnan Bauchi A PDP Ya Janye.

0

Jam’iyyar PDP a jihar Bauchi na shirin gudanar da sabon zaben fidda gwani na gwamna bayan da dan takarar gwamna na jam’iyyar, Kassim Ibrahim Mohammed ya janye.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilin jaridar LEADERSHIP a wannan Talatar, sakataren yada labarai na jam’iyyar a jihar Alhaji Yayanuwa Zainabari ya bayyana cewa dan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP bisa radin kansa ya janye daga takarar gwamna a 2023.

A cewar Zainbari, za a gudanar da sabon zaben fidda gwani a ranar Asabar.

Idan dai ba a manta ba, Mohammed shi ne dan takarar gwamna daya tilo a zaben fidda gwani na jam’iyyar, inda ya tara dukkan kuri’un wakilai 655 baya ga daya da ta yi dameji, wanda hakan ya bashi damar zama dan takarar gwamna a makon jiya.

Mohammed, wanda shi ne tsohon sakataren gwamnatin jihar, ya shiga takarar gwamnan Bauchi ne bayan gwamna mai ci Bala Mohammed ya zabi takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

Sai dai Gwamna Mohammed ya sha kaye a zaben fidda gwani na shugaban kasa da aka gudanar a Abuja a karshen makon da ya gabata.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *