September 17, 2026

Buhari Ya Tafi Kallon ƙwallon Najeriya da Ghana

0

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tafi kallon ƙwallon kafa da Najeriya za ta fafata da Ghana a Abuja a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya a Qatar.

Titin da ya fito daga fadar shugaban ƙasar har zuwa filin ƙwallon kafa da ke birnin Abuja ya kasance shiru babu ababen hawa saboda wucewar shugaban.

Gwamnati ta samar da tikitin shiga kallon wasan kyauta ga ƴan Najeriya domin nuna goyon baya ga ƴan wasan Najeriya.

Duk ƙasar da aka ci tsakanin Najeriya da Ghana ba za ta tafi gasar cin kofin duniya ba.

BBC Hausa

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *