September 19, 2026

Gwamnatin jihar Katsina Zata Kashe Naira Biliyan 16.7 wajen Sayan Takin Zamani ga Manoma

0

Gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ta amince da ware kudi har naira miliyan dubu sha shida da ɗari bakwai domin sayen takin zamani da za a rabawa manoma a jihar.

Kwamishinan ayyukan gona na jihar Katsina, Farfesa Ahmad Bakori ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron majalisar zartarwa a gidan gwamnatin jihar Katsina

Da yake yin bayani dalla-dalla Farfesa Ahmad Bakori ya ce ton dubu 20 na takin zamani zai kasance samfurin urea ton dubu shida sai kuma samfurin NPK 15-15 da NPK 10-10 ton dubu goma.

A cewar sa, harkar noma da samar da wadataccen abinci na daga cikin bangarorin da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya sanya a cikin mahimman abubuwa a gwamnatin sa.

Idan za a yi tunawa jihar Katsina na ɗaya daga cikin jahohin arewa maso yamma da suke samar da kaso mafi tsoka a bangaren noma.

Sai dai jihar da kuma yankin na fuskantar ƙalubalen tsaro shekara da shekaru wanda hakan tasa yanzu ba a iya noma rabin abinda ake noma ada.

Shin ko wannan ƙoƙari na gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗɗa zai taimaka wajen farfaɗo da harkokin noma da kiwo a wannan jiha ta Katsina, lokaci ne zai nuna.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *