September 18, 2026

Ƙungiyar K34 Na Kiran Dakta Mustapha Inuwa Da Ya Tsaya Takarar Gwamna 2023.

0

Wata Ƙungiya mai zaman kanta tayi kiran Dr Mustapha Muhd Inuwa Sakataren gwamnatin Jahar Katsina daya fito takarar gwamnan Katsina a 2023 domin karasa ayyukan da mai girma gwamna Masari ya fara.

Wannan kiran yana fitowa ta bakin shugaban Ƙungiyar Alh Abubakar Tsanni a wata zantawa da sukayi da jaridar Katsina post a ranar Lahadi nan, inda ya bayyana cewa zasu tsaya-tsayin daka domin samun nagartaccen mutum wanda zai karasa ayyukan da gwamnatin ta fara.

“Ya rike Sakataren gwamnati har sau 3 sannan yayi ciyaman na jam’iyya gamida kwashinan ilimi ba’a taba samun sa da wani almubazzaranci ba” inji Dr Tsanni.

Tsanni ya kara da bayyana Cewa Ƙungiyar su bazata bari A rasa irin wannan haziki gwamnatin Jahar ba.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *