Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Yana Ba ‘Yan Ta’adda Sa’a A Katsina.
Rundunar yan sandan Najeriya ta samu nasarar kama wanda ake zargi yana ba ‘yan ta’adda sa’a da ke addabar jihohin Katsina, Kaduna da kuma Zamfara.
Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar Katsina SP Gambo Isah ya fitar.
Sanarwar ta ce an kama mutumin mai suna Sani Bello ɗan kimanin shekaru 53 da haihuwa da ke zaune akan titin Maiduguri, cikin ƙaramar hukumar Sabuwa da ke jihar Katsina.
A lokacin da ake gudanar da bincike, an samu rigunan kariya daga harbin bindiga 4 na gida da aka haɗa su kayan tsafi a hannunsa.
Haka kuma sanarwar ta ce, ya amsa da bakinsa cewa yana ba yan ta’adda sa’a ta hanyar ba su layu da ƙirina da kuma yi masu addu’a don samun nasara a cikin ayyukansu na ta’addanci.
Kuma ya ce, “ina sayar da kowace rigar kariya daga harbin bindiga akan kuɗi naira ₦60,000.
Kama Mutunen dai ya biyo bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi a ranar 26/11/2022 da misalin karfe 06:00am.
Rundunar ƴan sandan ta kuma kama wasu da ake zargin yan fashi ne dake addabar garin Katsina da ayyukan ta’addanci.
Sanarwar ta ce mutanen da aka kama sun haɗa da: Usman Umar da aka fi sani da SHARBULO ɗan kimanin shekaru 28 da haihuwa dake unguwar Kofar Marusa cikin garin Katsina da kuma Musa Isiyaku da aka fi sani da Danmusa ɗan kimanin shekaru 20 da haihuwa dake unguwar Kofar Marusa cikin garin Katsina.
Sauran su ne Shamsu Umar da aka fi sani da BAKIN WAKE mai shekaru 29 dake unguwar Maɗacin Ƴan-Nono cikin garin Katsina, Sanusi Ibrahim da aka fi sani da AJI, mai shekaru 28 da ke unguwar Kofar Kaura cikin garin Katsina, sai kuma Yakubu Kabir da aka fi sani da MAKURI mai shekaru 20 da haihuwa da ke unguwar Kofar Marusa cikin garin Katsina.
A lokacin da ake gudanar da bincike, an samu wayar salula 4, adduna 2, takobi, ƙananan wuƙaƙe, fincis da kuma cisel a hannunsu.
Kama su dai ya biyo bayan samun kiran gaggawa da rundunar ta yi a ranar 16/11/2022 da misalin karfe 04:00 cewa, suna sheƙe ayarsu a unguwar Dutsen Amare da ke cikin garin Katsina.
Kuma yan sandan suka je wurin, tare da samun nasarar kama su.
Sauran mutanen da rundunar ta kama sun haɗa da waɗanda ake zargin masu satar babura da sayar da kayan maye ne.
