‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Ofishin Yan Sanda, Sun Sako Wadanda Aka Tsare, Sun Yi Awan Gaba Da Makamai A Anambra.
A jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari ofishin ‘yan sanda na unguwar Ihiala a karamar hukumar Ihiala ta jihar Anambra, inda suka banka mashi wuta.
Hakanan kuma, ‘yan bindigar, sun kubutar da wasu da ake tsare da su a ofishin yan sandan, tare da kutsawa cikin dakin ajiyar makamai na ofishin, inda suka kwashe makamai da alburusai.
A cewar wasu majiyoyi, ‘yan bindigar sun kai farmaki yankin ne da sanyin safiyar Laraba, inda suka bude wuta kan ‘yan sandan dake bakin aiki, amma ‘yan sandan sun maida masu biki ta hanyar far masu da harbin bindiga.
An bada rohoton cewa, ‘yan bindigar sun jefa bama-bamai a cikin ofishin yan sandan, lamarin da ya sa ginin ya kone, amma ba a samu asarar rai ba.
Don taimakawa wajen kashe gobarar, saida aka tura ‘yan kwana-kwana.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Anambrar DSP Toochukwu Ikenga, ya tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ya ce ‘yan sandan dake bakin aiki sun samu nasarar fatattakar ‘yan ta’addan, inji majiyar Popular News Hausa ta jaridar Sunnews.
Ya bayyana cewa, an samu bindiga kirar AK-47 guda ɗaya da ‘yan bindigar da suka gudu suka yadda a inda aka kai harin.
“Yan bindigar sun tsere ne daga wurin saboda yadda jami’an ‘yan sandan suka ci karfinsu da harbe-harbe ba tare da samun asarar rai ba.”
“Abin takaici, bama-baman da ‘yan bindigar suka jefa a cikin ginin ofishin ‘yan sanda tuni suka ƙone ginin” , inji shi.
