September 18, 2026

Masari Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Daga Darajar Asibitin Kafur.

0

Gwamnan jihar Katsina ya kai ziyarar duba aikin daga darajar asibitin Kafur zuwa babbar asibiti.

Injiniyan dake kula da aikin Architech Maliki ne ya zagaya da gwamna Aminu Bello Masari a lokacin ziyarar domin duba aikin.

Da yake yima gwamnan jawabi, injiniyan dake kula da aikin ya ce yanzu haka ana zamanantarwa, ginawa da kuma daga darajar gine-ginen ta.

Abinda ya ce zai bata damar yin ayyuka kamar na manyan asibitoci.

Injiniyan ya ce an rushe muhimman gine-ginen asibitin, tare da samar da karin wuri domin fadada ta.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *