Gwamnatin Jihar Katsina Ta Raba Buhunnan Shinkafa Da Tsabar Kuɗi A Danja, Bindawa Da Kankia.
Gwamnatin jihar Katsina ta raba buhunnan shinkafa da Naira 5,000 ga mutane masu ƙaramin ƙarfi a matsayin tallafin Sallah a ƙaramar hukumar Danja.
Kwamishinan kula da harkokin addinai Isyaku Dabai da babban sakataren ma’aikatar yaɗa labarai Abubakar Ammani Balarabe suka duba yadda rabon kayan ya gudana a sakatariyar ƙaramar ta Danja.
Da yake magana a lokacin rabon kayan, kwamishinan ya bayyana cewa jimullar mutane masu ƙaramin ƙarfi sama da 950 ne suka amfana tallafin.
Isyaku Dabai ya ce samar da shinkafar nada nufin taimaka ma mutanen don suyi hidimar Sallah cikin jindaɗi.
Kwamishinan ya yi nuni da cewa gwamnatin Dikko Radda na ƙoƙari wajen bunƙasa jindaɗin mutane masu ƙaramin ƙarfi, tara da samar masu da romon demokradiyya.
Isyaku Dabai ya bayyana abincin buɗa-bakin da gwamnati mai ci yanzu ke rabawa a matsayin abun cigaba.
A jawabanshi, babban sakataren ma’aikatar yaɗa labarai Abubakar Ammani Balarabe ya yaba ma Dikko Radda bisa samar da kayan tallafin, tare da yin kira ga waɗanda suka amfana kayan suyi addu’ar ganin gwamnati mai ci yanzu ta samu nasara.
Wasu daga cikin waɗanda suka amfana da kayan, sun gode ma gwamnan, tare yin kira cewa, kada yayi ƙasa-a-gwiwa wajen cigaba da yin irin wannan aikin.
A wani labarin kuma, ƙananan hukumomin Kankia da Bindawa sun raba buhunnan shinkafa da tallafin tsabar kuɗi ga mutane masu ƙaramin ƙarfi a yankunan.
Da suke magana a lokacin rabon kayan, shugabannin ƙananan hukumomin biyun Musa Maikuɗi da Badaru Musa Giremawa sun ce an ba waɗanda suka amfana da tallafin shinkafa da Naira 5,000 kamar yadda gwamnatin jiha ta samar da su a matsayin tallafin azumi da na Sallah.
Kamar yadda suka bayyana, an ba kowace ƙaramar hukuma buhunnan shinkafa 1,000 da kuma tsabar kuɗi domin raba su ga mutane masu ƙaramin ƙarfi don ganin sun yi azumi da Sallah cikin daɗi
Musa Maikuɗi da Badaru Musa sun shawarci waɗanda suka samu tallafin suyi amfani da shi yadda yakamata, tare da yin addu’ar neman zaman lafiya ga yankunansu dama jiha baki ɗaya.
A jawabansu na daban daban, shugabannin kwamitocin rabon kayan tallafin na kananan hukumomin Bishir Abubakar Kafin Soli da Ahmed Musa Bindawa sun bayyana tallafin a matsayin wanda ya zo kan kari.
Itama da take magana, wata memba ta kwamitin rabon kayan Zainab Hadi Kankia ta shawarci waɗanda suka amfana da cewa kada su sayar da su.
