Matsalar Sha Da Fataucin Miyagun kwayoyi Ciwo Ne Na Kowa Da Kowa. -Hon. Musa Adamu Funtua
Kwamishinan muhalli na jihar Katsina Honarabul Musa Adamu Funtua ya bayyana cewa matsalar shan kwaya da fataucin ta, ciwo ne da ya shafi kowa da kowa a cikin al’umma
Hon. Musa Adamu ya bayyana haka a lokacin da tawagar Anti-Drugs Campaign Network suka kai masa ziyara a ofishin sa da ke Katsina.
Kwamishinan wanda ya ce ma’aikatar muhalli tana da rawar da zata taka wajen ganin an samu saukin wannan masifa ta sha da fataucin miyagun kwayoyi musamman a tsakanin matasa waɗanda sune ƙashin bayan al’umma.

Haka kuma ya ƙara da cewa wannan abu ciwon kowa da kowa ne, mutum ɗaya ko biyu ba za su iya yi ba, ya ƙara da cewa wannan tunani ne mai kyau da aka samar da irin wannan tafiya da zata tunkari irin waɗannan matsaloli a cikin al’umma.
“Yanzu wani abu da muke sakaci da shi, shi ne wani zai zo cikin al’umma ya buɗe ƙyamis sai ka ji an ce yana da kirki, alhali kuwa yana cutar da jama’a ta hanyar sayarwa da yara kwaya, saboda haka dole sai an sanya lura so sai” inji shi
Alhaji Musa Adamu Funtua ya ja hankalin al’umma da cewa sune da kansu za su sa lura ga duk wanda ke sayar da kwaya a cikin su, kadda a nuna jin kunya ko nauyi wajen maganin wannan matsala.

Tunda farko a jawabinta shugabar kungiyar Anti-Drugs Campaign Network’Khadija Suleiman Saulawa ta bayyana cewa tununin kafa wannan tafiya ya biyo bayan wani rahoto da ke cewa a jihohin arewa, jihar Katsina ce ta biyu wajen sha da fataucin ƙwayoyi.
Ta ƙara da cewa bayyana wannan rahoto ya tada hankalin su, da duk wani mai kishin jihar Katsina da ma arewa baƙi ɗaya. Ta cigaba da cewa ya zame masu dole su yi abinda suke Iya yin don ganin an rage wannan bala’i da ya shigo al’umma.

Tana mai cewa sun kai ziyarori wurare daban-daban domin samun shawara da haɗin gwiwa wajen tunkarar matsalar baƙi ɗaya, daga cikin wuraren da suka kai ziyarar sun haɗa ya hukumar NDLEA da NIS da Masarautar Katsina da sauran wurare.
Shima da yake nasa ta’aliki Malam Ibrahim Sogiji wanda shine kodinata da wannan tafiya ya ce sun yi tsari mai kyau wajen ganin tunkarar wannan matsala.
Ya ƙara da cewa har littafin sun samar wanda yake nuna tarihin shaye-shayan a wannan lardi na Katsina da sauran abubuwa sannan ya ce sun tsara jadawalin wayar da kan al’umma da yin kira ga hukumomi da masu ruwa da tsaki domin a cimma nasara.
