September 18, 2026

Karya Ne Ba a Kashe Mutune 17 A Malumfashi Ta Jihar Katsina Ba – Rundunar ‘Yan Sanda

0

Rundunar Yan sanda a Jihar Katsina ta musanta rahoton kai hari da halaka mutane 17 a kauyen karfi dake karamar hukumar Malumfashi.

A tabakin kakakin rundunar ta Yan sanda a Jihar Katsina SP Isa Gambo yace labarin na kanzon kurege ne kawai.

SP Gambo yace sun tuntubi Jami’in dake kula da rundunar ta Yan sanda a Malumfashi akan lamarin inda ya tabbatar masu da babu makamancin wannan hari a kauyen da kuma halaka mutane 17.

Kamar yadda kakakin rundunar yace al’umma su guji yada labarai wadanda basu da sahihanci gudun hargitsa zaman lafiyar al’umma.

About The Author

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *