Me ya biyo Bayan Ganawar Shugaba Buhari da Dattawan Jihar Katsina?
Gwamna Aminu Bello Masari ya jagoranci tawagar wakilan Dattawan jihar Katsina domin ganawa da Shugaba Muhammadu Buhari a kan al’amuran da suka shafi jihar, musamman tsaro da kuma Asibitin Koyarwa na Jami’ar Umar Musa Yar’adua dake Katsina.
A cikin wannan tawaga akwai Ministan Zirga-zirgar jiragen sama Sanata Hadi Sirika, Sanata Mamman Abubakar Danmusa, Sanata Abba Ali, da Alhaji Yusuf Nalado. Haka kuma a wannan zama akwai Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban kasa Ambasada Ibrahim Gambari da Ministan Lafiya Dokta Osagie Ehanire.
Credit AbdulHadi Ahmad Bawa SSA Social Media
Photo fadar shugaban Kasa
