September 17, 2026

Zamu Yi Aiki Tare Da Kungiyar Haɗin Kan Mutanen Funtua Wajen Samarwa Da Matasa Aikin Yi. -Hon. Ya’u NOA

IMG-20250305-WA0005

Zamu Yi Aiki Tare Da kungiyar Haɗin Kan Mutanen Funtua Wajen Samarwa Da Matasa Aikin Yi. -Hon. Ya’u NOA

Mai baiwa gwamna shawara akan harkokin samar da guraben ayyukan Hon. Ya’u NOA ya bayyana cewa ma’aikatar sa zata yi aiki tare da kungiyar haɗin Kan Mutanen Funtua Wato ” Funtua Unity Foundation”

Hon. Ya’u NOA ya bayyana haka a lokacin da kungiyar ta kai masa ziyarar ban girma a ofishin sa ƙarƙashin jagorancin kwamared Mannir Suleiman a Katsina

Haka kuma Hon. Ya’u NOA ya ƙara da cewa ma’aikatar ta samar da guraben ayyukan yi da cigaba zata kirkiri wani haɗin gwiwa da kungiyar haɗin Kan Mutanen Funtua domin samarwa da matasa aiki.

A cewar sa, ko shakka babu wannan kungiyar an samar da ita a lokacin da ya da ce domin ko ba komai zata tallafawa matasan yankin Funtua wajen sama masu damamaki musamman ayyukan yi.

Alhaji Ya’u NOA wanda ya bayyana cewa, an samu damamaki da dama na ayyukan ‘yan sanda da sojoji da wasu hukumomin tsaro amma saboda rashin wayar da kan matasa akan mahimmancin shiga aikin dole tasa aka rasa guraben.

Kazalika mai baiwa gwamna shawarar ya ce za su yi hadin gwiwa da kungiyar wajen ganin ta samarwa da matasa aiki yi a matakin jiha da kuma ƙasa baki ɗaya.

Tunda farko da yake jawabi, shugaban kungiyar haɗin Kan Mutanen Funtua Kwamared Mannir Suleiman ya bayyana cewa dalilin kai wannan ziyara shi ne domin su samar da Hon. Ya’u NOA irin ayyukan wannan gidauniya.

A cewar sa, babban abinda wannan kungiyar tasa gaba shine ganin an samar da hadin kai da cigaban tare inganta harkokin da suka shafi ilimi da kiwon lafiya da kuma ayyukan jin kai a tsakanin al’ummar Funtua.

Haka kuma shugaban kungiyar ya nanata kudirin wannan gidauniya na ganin sun haɗa kai da hukumomin gwamnati da kuma waɗanda ba na gwamnati ba domin samar na cigaba a yankin Funtua.

Kwamared Mannir Suleiman ya yabawa gwamnatin jihar Katsina ƙarkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa akan irin ayyukan raya ƙasa da take yi a faɗin jihar baƙi ɗaya.

Alhaji Mannir Suleiman ya yi kira ga jama’a da su goyi bayan shirye-shirye da tsare-tsaren gwamnati domin cimma manufar da ake buƙata

About The Author